ترجمة سورة الرحمن

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة الرحمن باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Ar-Rahman


(Allah) Mai rahama.

Yã sanar da Alƙur'ani.

Yã halitta mutum.

Yã sanar da shi bayãni (magana).

Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Mãsu rassan itãce.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Mãsu duhun inuwa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
سورة الرحمن
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (الرَّحْمن) من السُّوَر المكية، وقد أبانت عن مقصدٍ عظيم؛ وهو إثباتُ عموم الرحمة لله عز وجل، وقد ذكَّر اللهُ عبادَه بنِعَمه وآلائه التي لا تُحصَى عليهم، وفي ذلك دعوةٌ لاتباع الإله الحقِّ المستحِق للعبودية، وقد اشتملت السورةُ الكريمة على آياتِ ترهيب وتخويف من عقاب الله، كما اشتملت على آياتٍ تُطمِع في رحمةِ الله ورضوانه وجِنانه.

ترتيبها المصحفي
55
نوعها
مكية
ألفاظها
352
ترتيب نزولها
97
العد المدني الأول
77
العد المدني الأخير
77
العد البصري
76
العد الكوفي
78
العد الشامي
78

* سورة (الرَّحْمن):

سُمِّيت سورة (الرَّحْمن) بهذا الاسم؛ لافتتاحها باسم (الرَّحْمن)، وهو اسمٌ من أسماءِ الله تعالى.

* ذكَرتْ سورةُ (الرحمن) كثيرًا من فضائلِ الله على عباده:

عن جابرِ بن عبدِ اللهِ رضي الله عنهما، قال: «خرَجَ رسولُ اللهِ ﷺ على أصحابِه، فقرَأَ عليهم سورةَ الرَّحْمنِ، مِن أوَّلِها إلى آخِرِها، فسكَتوا، فقال: «لقد قرَأْتُها على الجِنِّ ليلةَ الجِنِّ فكانوا أحسَنَ مردودًا منكم! كنتُ كلَّما أتَيْتُ على قولِه: {فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ}، قالوا: لا بشيءٍ مِن نِعَمِك رَبَّنا نُكذِّبُ؛ فلك الحمدُ!»». أخرجه الترمذي (٣٢٩١).

1. من نِعَم الله الظاهرة (١-١٣).

2. نعمة الخَلْق (١٤-١٦).

3. نِعَم الله في الآفاق (١٧-٢٥).

4. من لطائف النِّعَم (٢٦-٣٢).

5. تحدٍّ وإعجاز (٣٣-٣٦).

6. عاقبة المجرمين (٣٧-٤٥).

7. نعيم المتقين (٤٦-٧٨).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (7 /550).

مقصدُ سورة (الرَّحْمن) هو إثباتُ الرحمةِ العامة لله عز وجل، الظاهرةِ في إنعامه على خَلْقه، وأعظمُ هذه النِّعَم هو نزول القرآن، وما تبع ذلك من نِعَم كبيرة في هذا الكون.

يقول الزَّمَخْشريُّ: «عدَّد اللهُ عز وعلا آلاءه، فأراد أن يُقدِّم أولَ شيءٍ ما هو أسبَقُ قِدْمًا من ضروب آلائه وأصناف نَعْمائه؛ وهي نعمة الدِّين، فقدَّم من نعمة الدِّين ما هو في أعلى مراتبِها وأقصى مَراقيها؛ وهو إنعامُه بالقرآن وتنزيلُه وتعليمه؛ لأنه أعظَمُ وحيِ الله رتبةً، وأعلاه منزلةً، وأحسنه في أبواب الدِّين أثرًا، وهو سَنامُ الكتب السماوية ومِصْداقها والعِيارُ عليها.

وأخَّر ذِكْرَ خَلْقِ الإنسان عن ذكرِه، ثم أتبعه إياه؛ ليعلمَ أنه إنما خلَقه للدِّين، وليحيطَ علمًا بوحيِه وكتبِه وما خُلِق الإنسان من أجله، وكأنَّ الغرض في إنشائه كان مقدَّمًا عليه وسابقًا له، ثم ذكَر ما تميَّز به من سائر الحيوان من البيان؛ وهو المنطقُ الفصيح المُعرِب عما في الضمير». "الكشاف" للزمخشري (4 /443).