ترجمة سورة المرسلات

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة المرسلات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Al-Mursalat


Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.

Sa'an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.

Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.

sa'an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.

Sa'an nan da malã'iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.

Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.

Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne

To, idan taurãri aka shãfe haskensu.

Kuma, idan sama aka tsãge ta.

Kuma, idan duwãtsu aka nike su.

Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su.

Domin babbar rãnar da aka yi wa ajali.

Domin rãnar rarrabẽwa.

Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabẽwa?

Bone yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Ashe, ba Mu halakar da (mãsu ƙaryatãw) na farko ba.

Sa'an nan, kuma zã Mu biyar musu da na ƙarshe?

Haka nan, Muke aikatãwa da mãsu yin laifi.

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

Ashe, ba Mu halitta ku daga wani ruwa wulakantacce ba.

Sa'an nan Muka sanya shi a cikin wani wurin natsuwa amintacce.

Zuwa ga wani gwargwadon mudda sananna.

Sa'an nan, Muka nũna iyãwarMu? Madalla da Mu, Mãsu nũna iyãwa.

Bone ya tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba.

Ga rãyayyu da matattu,

Kuma, Muka sanya, a cikinta, kafaffun duwãtsu maɗaukaka, kuma Muka shayar da ku ruwa mai dãɗi?

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi!

Ku tafi zuwa ga wata inuwa mai rassa uku.

Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadãtarwa daga harshen wuta.

Lalle ne, ita, tanã jifã da tartsatsi kamar sõraye.

Kamar dai su raƙumma ne baƙãƙe.

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Wannan, yini ne da bã zã su iya yin magana ba.

Bã zã a yi musu izni ba, balle su kãwo hanzari.

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Wannan rãnar rarrabẽwa ce, Mun tattara ku tare da mutãnen farko.

To, idan akwai wata dabara gare ku, sai ku yi ma Ni ita.

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Lalle ne, mãsu taƙawa suna a cikin inuwõwi da marẽmari.

Da wasu 'ya'yan itãce irin waɗanda suke marmari.

(A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni'ima sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa."

Lalle ne, Mũ haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

(Ana ce musu) "Ku ci ku ji ɗan dãdi kaɗan, lalle ne dai ku mãsu laifi ne."

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Kuma, idan an ce musu: "Ku yi rukũ'i; bã zã su yi rukũ'in (salla) ba."

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

To, da wane lãbãri (Littãfi), waninsa (Alƙur'ãni) zã su yi ĩmãni
سورة المرسلات
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (المُرسَلات) من السُّوَر المكية، نزلت بعد سورة (الهُمَزة)، وقد جاءت ببيانِ قدرة الله على بعثِ الناس بعد هلاكهم؛ فهو المتصفُ بالرُّبوبية والألوهية، وقد افتُتحت بمَشاهدِ القيامة، والتذكير بمَصارعِ الغابرين، وذكَرتْ تأمُّلات في خَلْقِ الإنسان والكون؛ ليعودَ الخلقُ إلى أوامرِ الله، وليستجيبوا له سبحانه، و(المُرسَلات): هي الرِّياحُ التي تهُبُّ متتابِعةً.

ترتيبها المصحفي
77
نوعها
مكية
ألفاظها
181
ترتيب نزولها
33
العد المدني الأول
50
العد المدني الأخير
50
العد البصري
50
العد الكوفي
50
العد الشامي
50

* سورة (المُرسَلات):

سُمِّيت سورة (المُرسَلات) بذلك؛ لافتتاحها بالقَسَمِ الإلهيِّ بـ(المُرسَلات)؛ وهي: الرِّياح التي تهُبُّ متتابِعةً.

سورة (المُرسَلات) من السُّوَر التي شيَّبتْ رسولَ الله صلى الله عليه وسلم:

عن ابنِ عباسٍ رضي الله عنهما، قال: «قال أبو بكرٍ الصِّدِّيقُ رضي الله عنه لرسولِ اللهِ صلى الله عليه وسلم: يا رسولَ اللهِ، أراكَ قد شِبْتَ! قال: «شيَّبتْني هُودٌ، والواقعةُ، والمُرسَلاتُ، و{عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ}، و{إِذَا اْلشَّمْسُ كُوِّرَتْ}». أخرجه الحاكم (3314).

1. مَشاهد القيامة (١-١٥).

2. مَصارع الغابرين (١٦-١٩).

3. تأمُّلات في خَلْقِ الإنسان والكون (٢٠-٢٨).

4. عودٌ لمَشاهد القيامة (٢٩-٥٠).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (8 /540).

مقصدُ سورة (المُرسَلات): الاستدلالُ على وقوع البعث بعد فَناء الدنيا، والاستدلال على إمكانِ إعادة الخَلْقِ بما سبَق من خَلْقِ الإنسان وخلق الأرض، وفي ذلك دلائلُ على قدرة الله، واتصافِه بالوَحْدانية والرُّبوبية.

ينظر: "التحرير والتنوير" لابن عاشور (29 /419).