ترجمة سورة المعارج

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة المعارج باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Al-Ma'arij


Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

Daga Allah Mai matãkala.

Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

Da matarsa da ɗan'uwansa.

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

Mai twãle fãtar goshi.

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

Sai mãsu yin salla,

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
سورة المعارج
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (المعارج) من السُّوَر المكية، نزلت بعد سورة (الحاقة)، وقد أكدت وقوعَ يوم القيامة بأهواله العظيمة، التي يتجلى فيها جلالُ الله وعظمته، وقُدْرتُه الكاملة على الجزاء، وأن مَن استحق النار فسيدخلها، ومَن أكرمه الله بجِنانه فسيفوز بذلك، وخُتمت ببيانِ جزاء مَن آمن، وتهديدٍ شديد للكفار؛ حتى يعُودُوا عن كفرهم.

ترتيبها المصحفي
70
نوعها
مكية
ألفاظها
217
ترتيب نزولها
79
العد المدني الأول
44
العد المدني الأخير
44
العد البصري
44
العد الكوفي
44
العد الشامي
43

* سورة (المعارج):

سُمِّيت سورة (المعارج) بهذا الاسم؛ لوقوع لفظ (المعارج) فيها؛ قال تعالى: {مِّنَ اْللَّهِ ذِي اْلْمَعَارِجِ} [المعارج: 3]، قال ابنُ جريرٍ: «وقوله: {ذِي اْلْمَعَارِجِ} يعني: ذا العُلُوِّ، والدرجاتِ، والفواضلِ، والنِّعمِ». " جامع البيان" للطبري (29 /44).

1. المقدمة (١-٥).

2. مُنكِرو البعث (٦-٢١).

3. المؤمنون بالبعث (٢٢-٣٥).

4. هل يتساوى الجزاءانِ؟ (٣٦-٤١).

5. تهديدٌ شديد (٤٢-٤٤).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (8 /343).

يقول ابن عاشور عن مقصدها: «تهديدُ الكافرين بعذاب يوم القيامة، وإثباتُ ذلك اليوم، ووصفُ أهواله.
ووصفُ شيء من جلال الله فيه، وتهويلُ دار العذاب - وهي جهنَّمُ -، وذكرُ أسباب استحقاق عذابها.
ومقابلةُ ذلك بأعمال المؤمنين التي أوجبت لهم دارَ الكرامة، وهي أضدادُ صفات الكافرين.
وتثبيتُ النبيِّ صلى الله عليه وسلم، وتسليتُه على ما يَلْقاه من المشركين.
ووصفُ كثيرٍ من خصال المسلمين التي بثها الإسلامُ فيهم، وتحذير المشركين من استئصالهم وتبديلهم بخيرٍ منهم». "التحرير والتنوير" لابن عاشور (29 /153).