ترجمة سورة البلد

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة البلد باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Al-Balad


Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

Da mahaifi da abin da ya haifa.

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

Da harshe, da leɓɓa biyu.

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

Ita ce fansar wuyan bãwa.

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

Ga marãya ma'abũcin zumunta.

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

Waɗannan ne ma'abũta albarka

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.
سورة البلد
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (البَلَد) من السُّوَر المكية، وقد افتُتحت بالقَسَم بـ(البَلَد الحرام)، وهو (مكَّة المكرَّمة)، موطنُ نشأة النبي صلى الله عليه وسلم؛ وذلك تكريمًا للنبي صلى الله عليه وسلم، ورفعًا لشأنه، واشتملت السورةُ الكريمة على تثبيتِ المسلمين، وسُنَّةِ الله في هذه الحياة؛ من المكابدة والمشقَّة وعدم الراحة، وبيَّنتْ طريقَيِ الخير والشر؛ داعيةً إلى توحيد الله، واتباع طريق الخير.

ترتيبها المصحفي
90
نوعها
مكية
ألفاظها
82
ترتيب نزولها
35
العد المدني الأول
20
العد المدني الأخير
20
العد البصري
20
العد الكوفي
20
العد الشامي
20

* سورة (البَلَد):

سُمِّيت سورة (البَلَد) بهذا الاسم؛ لافتتاحها بقَسَمِ الله بـ(البَلَد الحرام)؛ قال تعالى: {لَآ أُقْسِمُ بِهَٰذَا اْلْبَلَدِ} [البلد: 1].

1. خلقُ الإنسان في كَبَدٍ (١-٤).

2. تكليف الإنسان وضعفُه (٥-٢٠).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /135).

غرضُ السورة هو التنويه بـ(مكَّة المكرَّمة)، وبمُقام النبي صلى الله عليه وسلم فيها، والتذكيرُ بأسلاف النبي صلى الله عليه وسلم من الأنبياء، وذمُّ الشرك وأهله.

ينظر: "التحرير والتنوير" لابن عاشور (30 /346).