ترجمة سورة الفجر

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة الفجر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Al-Fajr


Inã rantsuwa da alfijiri.

Da darũruwa gõma.

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

Da dare idan yana shũɗewa.

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

Da Fir'auna mai turãku.

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

Yã kai rai mai natsuwa!

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).
سورة الفجر
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (الفجر) من السُّوَر المكية، نزلت بعد سورة (الليل)، وقد افتُتحت بقَسَمِ الله عز وجل بـ(الفجر)، وجاءت على ذكرِ ما عذَّب اللهُ به عادًا وثمودَ وقوم فرعون؛ ليعتبِرَ بذلك مشركو قريش، وفي ذلك تثبيتٌ للنبي صلى الله عليه وسلم على طريق الدعوة، وخُتمت السورة الكريمة بتقسيم الناس إلى أهل الشقاء وأهل السعادة.

ترتيبها المصحفي
89
نوعها
مكية
ألفاظها
139
ترتيب نزولها
10
العد المدني الأول
32
العد المدني الأخير
32
العد البصري
29
العد الكوفي
30
العد الشامي
30

* سورة (الفجر):

سُمِّيت سورة (الفجر) بهذا الاسم؛ لافتتاحها بقَسَمِ الله عز وجل بـ(الفجر)؛ قال تعالى: {وَاْلْفَجْرِ} [الفجر: 1].

1. في التاريخ عِبْرة وعِظة (١-١٤).

2. أهل الشقاء وأهل السعادة (١٥- ٣٠).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /127).

مقصدُ السورة هو إنذارُ قُرَيش بعذاب الآخرة عن طريقِ ضربِ المثَلِ في إعراضهم عن قَبول رسالة ربهم بمثَلِ عادٍ وثمودَ وقومِ فرعون، وما أوقَعَ اللهُ بهم من عذاب، وفي ذلك تثبيتُ النبي صلى الله عليه وسلم على هذه الدعوة.

ينظر: "التحرير والتنوير" لابن عاشور (30 /312).