ترجمة سورة التكوير

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة التكوير باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

An-Takwir


Idan rãna aka shafe haskenta

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

Mãsu gudu suna ɓũya.

Da dare idan ya bãyar da bãya.

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

Shin, a inã zã ku tafi?

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
سورة التكوير
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (التَّكْوير) من السُّوَر المكية، نزلت بعد سورة (المَسَد)، وهي من السُّوَر التي شيَّبتْ رسولَ الله صلى الله عليه وسلم؛ كما صح في الأثر؛ وذلك لِما أخبَرتْ عنه من الأهوال التي تسبق يومَ القيامة؛ تخويفًا للكفار من عذاب الله الواقع بهم إن بَقُوا على كفرهم، وقد خُتِمت بحقيقةِ الوحي، وإثباتِ مجيئه من عند الله عز وجل.

ترتيبها المصحفي
81
نوعها
مكية
ألفاظها
104
ترتيب نزولها
7
العد المدني الأول
29
العد المدني الأخير
29
العد البصري
29
العد الكوفي
29
العد الشامي
29

* سورة (التَّكْوير):

سُمِّيت سورة (التَّكْوير) بهذا الاسم؛ لافتتاحها بقوله تعالى: {إِذَا اْلشَّمْسُ كُوِّرَتْ} [التكوير: 1].

سورة (التَّكْوير) من السُّوَر التي شيَّبتْ رسول الله صلى الله عليه وسلم:

عن ابنِ عباسٍ رضي الله عنهما، قال: «قال أبو بكرٍ الصِّدِّيقُ رضي الله عنه لرسولِ اللهِ: يا رسولَ اللهِ، أراكَ قد شِبْتَ! قال: «شيَّبتْني هُودٌ، والواقعةُ، والمُرسَلاتُ، و{عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ}، و{إِذَا اْلشَّمْسُ كُوِّرَتْ}». أخرجه الحاكم (3314).

* سورة (التَّكْوير) من السُّوَر التي وصفت أحداثَ يوم القيامة بدقة؛ لذا كان النبي صلى الله عليه وسلم يدعو الصحابةَ إلى قراءتها:

عن عبدِ اللهِ بن عُمَرَ رضي الله عنهما، قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: «مَن سَرَّه أن ينظُرَ إلى يومِ القيامةِ كأنَّه رأيَ عينٍ، فَلْيَقرأْ: {إِذَا اْلشَّمْسُ كُوِّرَتْ}، و{إِذَا اْلسَّمَآءُ اْنفَطَرَتْ}، و{إِذَا اْلسَّمَآءُ اْنشَقَّتْ}». أخرجه الترمذي (٣٣٣٣).

1. حقيقة القيامة (١-١٤).

2. حقيقة الوحي (١٥-٢٩).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /49).

يقول ابنُ عاشور رحمه الله: «اشتملت على تحقيقِ الجزاء صريحًا، وعلى إثبات البعث، وابتُدئ بوصفِ الأهوال التي تتقدمه، وانتُقل إلى وصف أهوال تقع عَقِبَه.

وعلى التنويه بشأن القرآن الذي كذَّبوا به؛ لأنه أوعَدهم بالبعث؛ زيادةً لتحقيقِ وقوع البعث إذ رمَوُا النبيَّ صلى الله عليه وسلم بالجنون، والقرآنَ بأنه يأتيه به شيطانٌ». "التحرر والتنوير" لابن عاشور (30 /140).