ترجمة سورة النازعات

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة النازعات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

An-Nazi'at


Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

Da duwatsu, Yã kafe ta.

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

To, amma wanda ya yi girman kai.

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

Me ya haɗã ka da ambatonta?

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
سورة النازعات
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (النَّازعات) من السُّوَر المكية، وقد افتُتحت بذكرِ الملائكة التي تَنزِع الأرواح؛ ليبعثَ اللهُ الناس بعد ذلك في يوم الطامَّة الكبرى؛ ليكونَ من اتقى في الجِنان، ويذهبَ من طغى وآثر الحياةَ الدنيا إلى الجحيم مأواه، وقد ذكَّرت السورةُ الكريمة بنِعَمِ الله على خَلْقه وقوَّته وقهره بعد أن بيَّنتْ إقامةَ الحُجَّة على الكافرين، كما أقام موسى عليه السلام الحُجَّةَ على فرعون بالإبلاغ.

ترتيبها المصحفي
79
نوعها
مكية
ألفاظها
179
ترتيب نزولها
81
العد المدني الأول
45
العد المدني الأخير
45
العد البصري
45
العد الكوفي
46
العد الشامي
45

- قوله تعالى: {يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ اْلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا ٤٢ فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ} [النازعات: 42-43]:

عن عائشةَ رضي الله عنها، قالت: «كان النبيُّ صلى الله عليه وسلم يُسألُ عن الساعةِ حتى أُنزِلَ عليه: {يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ اْلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا ٤٢ فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ} [النازعات: 42-43]». أخرجه الحاكم (3895).

* سورة (النَّازعات):

سُمِّيت سورة (النَّازعات) بذلك؛ لافتتاحها بقَسَمِ الله بـ(النَّازعات)؛ وهم: الملائكةُ الذين ينتزعون أرواحَ بني آدم.

1. مَشاهد اليوم الآخِر (١-١٤).

2. قصة موسى عليه السلام مع فرعون (١٥-٢٦).

3. لفتُ النظر إلى خَلْقِ السموات والأرض (٢٧-٣٣).

4. أحداث يوم القيامة (٣٤-٤١).

5. سؤال المشركين عن وقتِ الساعة (٤٢-٤٦).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /23).

يقول ابنُ عاشور رحمه الله: «اشتملت على إثباتِ البعث والجزاء، وإبطال إحالة المشركين وقوعَه، وتهويلِ يومه، وما يعتري الناسَ حينئذٍ من الوَهَلِ، وإبطال قول المشركين بتعذُّرِ الإحياء بعد انعدام الأجساد». "التحرير والتنوير" لابن عاشور (30 /59).