ترجمة سورة عبس

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة عبس باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Abasa


Yã game huska kuma ya jũya bãya.

Sabõda makãho yã je masa.

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

Da inabi da ciyãwa.

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

Da uwarsa da ubansa.

Da mãtarsa da ɗiyansa.

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

Baƙi zai rufe su.

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
سورة عبس
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (عبَسَ) من السُّوَر المكية، وقد نزلت في عتابِ الله نبيَّه صلى الله عليه وسلم في إعراضه عن ابنِ أمِّ مكتومٍ الأعمى، بسبب انشغاله مع صناديدِ قريش، وهذا العتاب لتعليم النبي صلى الله عليه وسلم المقارنةَ بين المصالح والمفاسد، وإعلاءٌ من شأن النبي صلى الله عليه وسلم، كما جاءت السورة على ذكرِ آيات الله ونِعَمه على خَلْقِه؛ مذكِّرةً إياهم بيوم (الصاخَّة)، حين ينقسم الناس إلى أهل جِنان، وأهل نيران.

ترتيبها المصحفي
80
نوعها
مكية
ألفاظها
133
ترتيب نزولها
24
العد المدني الأول
42
العد المدني الأخير
42
العد البصري
41
العد الكوفي
42
العد الشامي
40

* قوله تعالى: {عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ ١ أَن جَآءَهُ اْلْأَعْمَىٰ ٢ وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ ٣ أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ اْلذِّكْرَىٰٓ} [عبس: 1-4]:

عن عُرْوةَ، عن عائشةَ أمِّ المؤمنين رضي الله عنها، قالت: «أُنزِلتْ في ابنِ أمِّ مكتومٍ الأعمى»، قالت: «أتى النبيَّ ﷺ، فجعَلَ يقولُ: يا نبيَّ اللهِ، أرشِدْني! قالت: وعند النبيِّ ﷺ رجُلٌ مِن عُظَماءِ المشركين، فجعَلَ النبيُّ ﷺ يُعرِضُ عنه، ويُقبِلُ على الآخَرِ، فقال النبيُّ ﷺ: «يا فلانُ، أتَرى بما أقولُ بأسًا؟»، فيقولُ: لا؛ فنزَلتْ: {عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ} [عبس: 1]». أخرجه ابن حبان (٥٣٥).

* سورة (عبَسَ):

سُمِّيت سورة (عبَسَ) بذلك؛ لقوله تعالى في أولها: {عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ} [عبس: 1].

1. عتابُ المُحبِّ (١-١٦).

2. تفكُّر وتدبُّر (١٧-٣٢).
3. يومَك.. يومَك (٣٣-٤٢).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /41).

عتابُ اللهِ نبيَّه صلى الله عليه وسلم عتابَ المُحبِّ؛ لتزكيةِ نفس النبي صلى الله عليه وسلم، ولتعليمه الموازنةَ بين مراتبِ المصالح والمفاسد، وفي حادثةِ عُبُوسِه صلى الله عليه وسلم في وجهِ الأعمى أوضَحُ الدلالة على ذلك.

ينظر: "مصاعد النظر للإشراف على مقاصد السور" للبقاعي (3 /157)، "التحرير والتنوير" لابن عاشور (30 /102).