ترجمة سورة الإنشقاق

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

ترجمة معاني سورة الإنشقاق باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation.

Al-Inshikak


Idan sama ta kẽce,

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

To, zã shi dinga kiran halaka!

Kuma ya shiga sa'ĩr.

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

Da watã idan (haskensa) ya cika.

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.
سورة الإنشقاق
معلومات السورة
الكتب
الفتاوى
الأقوال
التفسيرات

سورة (الانشقاق) من السُّوَر المكية، نزلت بعد سورة (الانفطار)، وقد افتُتحت ببيان ما يسبق يومَ القيامة من أهوالٍ، وجاءت على ذكرِ أحوال الناس عند لقاء الله، وفي جزائهم وتقسيمهم إلى صِنْفَينِ: صنفٍ آمن بهذا اليوم فهو من أهل الجنان، وصنفٍ كذَّب به فهو من أهل النيران.

ترتيبها المصحفي
84
نوعها
مكية
ألفاظها
109
ترتيب نزولها
83
العد المدني الأول
25
العد المدني الأخير
25
العد البصري
23
العد الكوفي
25
العد الشامي
23

* سورة (الانشقاق):

سُمِّيت سورة (الانشقاق) بهذا الاسم؛ لافتتاحها بقوله تعالى: {إِذَا اْلسَّمَآءُ اْنشَقَّتْ} [الانشقاق: 1].

* سورة (الانشقاق) من السُّوَر التي وصفت أحداثَ يوم القيامة بدقة؛ لذا كان النبيُّ صلى الله عليه وسلم يدعو الصحابةَ إلى قراءتها:

عن عبدِ اللهِ بن عُمَرَ رضي الله عنهما، قال: قال رسولُ اللهِ صلى الله عليه وسلم: «مَن سَرَّه أن ينظُرَ إلى يومِ القيامةِ كأنَّه رأيَ عينٍ، فَلْيَقرأْ: {إِذَا اْلشَّمْسُ كُوِّرَتْ}، و{إِذَا اْلسَّمَآءُ اْنفَطَرَتْ}، و{إِذَا اْلسَّمَآءُ اْنشَقَّتْ}». أخرجه الترمذي (٣٣٣٣).

1. من أهوال يوم القيامة (١-٥).

2. أحوال الإنسان عند لقاء ربه (٧-١٥).

3. أحوال الإنسان في هذه الحياة (١٦-٢٥).

ينظر: "التفسير الموضوعي لسور القرآن الكريم" لمجموعة من العلماء (9 /75).

إثباتُ هولِ يوم القيامة، وما يسبقه من أحداث، وتنعيمُ اللهِ أولياءَه يوم الحساب؛ لأنَّهم صدَّقوا بهذا اليوم وآمَنوا به، وعقاب الله لمن كفَر بهذا اليوم؛ لأنهم كانوا لا يُقِرُّون بالبعث والعَرْضِ على الملك الذي أوجَدهم وربَّاهم؛ كما يَعرِض الملوك عبيدَهم، ويحكُمون بينهم؛ فينقسمون إلى أهل ثواب، وأهل عقاب، واسمها (الانشقاق) دالٌّ على ذلك.

ينظر: "مصاعد النظر للإشراف على مقاصد السور" للبقاعي (3 /172).